2 Kings 21:6 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ya miƙa ɗansa hadaya ta ƙonawa, ya yi sihiri da tsubu, ya tuntuɓi masu duba da masu ruhohi. Ya aikata mugunta ƙwarai a gaban Ubangiji, ya sa Ubangiji ya yi fushi.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
مَنَسّٜىٰ يَمِيڧَ طَنْسَ هَدَايَ تَڧُواْنَاوَا؞ يَنَ دُوبَا، يَنَ دَبُواْ؞ يَنَ بِنْ مَاسُ حَطَكَيْ دَ رُوحُواْحِنْ مَتَتُّو؞ يَنَ كُمَيِنْ بُواْكَنْثِ؞ يَعَيْكَتَ مُغُنْتَا سُواْسَيْ أَعِدُوانْ يَهْوٜىٰهْ ، وَنْدَ يَسَا يَهْوٜىٰهْ يَيِ ڢُشِے سُواْسَيْ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ya miƙa ɗansa hadaya ta ƙonawa ya kuma aikata sihiri, ya yi dūba. Ya yi ma'amala da masu mabiya da mayu. Ya aikata mugunta ƙwarai a gaban Ubangiji, ya sa Ubangiji ya yi fushi.