2 Kings 22:14 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai Hilkiya firist, da Ahikam, Akbor, da Shafan, da kuma Asahiya suka je don su yi magana da annabiya Hulda, matan Shallum ɗan Tikba, ɗan Harhas, mai ajiyar tufafi. Tana zama a Urushalima, a Yanki na Biyu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ هِلْكِيَ ڢِرِسْتِ دَ أَهِكَمْ دَ عَكْبُوارْ دَ شَڢَنْ دَ أَسَيَ سُكَ تَڢِے سُكَيِ مَغَنَ دَ أَنَّبِيَ هُلْدَ؞ هُلْدَ مَاتَرْ شَلُّمْ، وَنْدَ يَكٜىٰ طَنْ تِݣُو جِيكَنْ هَرْهَسْ، مَيْ لُورَ دَ رِيغُنَنْ ڢِرِسْتُواْثِے؞ هُلْدَ تَنَ ذَمَ أَ سَابُوَرْ عُنْغُوَ تَ عُرُوشَلِيمَ؞ أَ نَنْ سُكَيِ مَغَنَ دَ عِتَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai Hilkiya firist, da Ahikam, da Akbor, da Shafan, da Asaya suka tafi wurin annabiya Hulda, matar Shallum ɗan Tikwa, wato jikan Harhas, mai tsaron ɗakin da ake ajiye tufafi. A Urushalima take zaune a sabuwar unguwa. Suka kuwa yi magana da ita.