2 Kings 22:17 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Domin sun yashe ni suka ƙona turare wa waɗansu alloli, suka tozarta ni da dukan gumakan da hannuwansu suka sassaƙa, fushina zai yi ƙuna a kan wannan wuri, ba kuwa zai huce ba.’
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
تُنْدَيَكٜىٰ مُتَنٜىٰنْ يَهُودَ سُنْ رَبُ دَنِے، سُنَ مِيڧَ هَدَايُنْ ڧُواْنَاوَا غَ وَطَنْسُ أَلُّواْلِ، دُواْمِنْ سُسَا إِنْيِ ڢُشِے سَبُواْدَ سُنْيِ سُجَّدَ غَ دُكَنْ أَيُّكَنْ حَنُّوَنْسُ؞ سَبُواْدَ حَكَ ڢُشِنَ ذَيْ ڧُونَ عَكَنْ بِرْنِنَّنْ كُمَ بَابُ أَبِنْدَ ذَيْ كَشٜىٰشِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
domin sun rabu da ni, sun ƙona turare ga gumaka don su tsokane ni in yi fushi da aikin hannuwansu. Saboda haka fushina zai ƙuna a kan wurin nan, ba kuwa zai huce ba.’