2 Kings 22:19 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Domin zuciyarka mai tuba ce, ka kuma ƙasƙantar da kanka a gaban Ubangiji sa’ad da ka ji abin da na faɗa game da wannan wuri da mutanen wurin, cewa za su zama la’antattu da kuma kango, domin kuma ka kece tufafinka, ka kuma yi kuka a gabana, na ji ka, in ji Ubangiji.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
«تُنْدَ كَكٜىٰ دَ ذُوثِيَا مَيْ تُوبَ كَكُمَ ڧَسْڧَنْتَرْ دَكَنْكَ أَغَبَنَ سَعَدَّ كَجِ أَبِنْدَ نَڢَطَا غَمٜىٰدَ بِرْنِنَّنْ دَ مَذَوْنَنْسَ، يَدَّ نَثٜىٰ مُسُ ذَنْ مَيْدَ وُرِنْ كُڢَيْ دَ كُمَ عَلَمَرْ لَعَنَ، كَيَاغٜىٰ رِيغُنَنْكَ كَيِ كُوكَا أَغَبَنَ، تُواْ، نِے يَهْوٜىٰهْ نَجِ أَدُّعَرْكَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
da yake zuciyarka mai tuba ce, ka kuma ƙasƙantar da kanka a gabana sa'ad da ka ji yadda na yi magana gāba da wannan wuri, da kuma mazaunansa, cewa zai zama kufai da la'ana, kai kuwa ka keta tufafinka, ka yi kuka a gabana, hakika na ji kukanka.