2 Kings 22:8 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Hilkiya babban firist ya ce wa Shafan magatakarda, “Na sami Littafin Doka a haikalin Ubangiji.” Sai ya ba wa Shafan, shi kuma ya karanta.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ هِلْكِيَ بَبَّنْ ڢِرِسْتِ يَثٜىٰ وَ شَڢَنْ مَرُبُوثِنْ سَرْكِے «نَا سَامِ نَطَطّٜىٰنْ لِتَّڢِنْ كُواْيَرْوَرْ مُوسَٰى عَثِكِنْ غِدَنْ يَهْوٜىٰهْ ؞» سَعَدَّ هِلْكِيَ يَبَا شَڢَنْ لِتَّڢِنْ، سَيْ شَڢَنْ يَكَرَنْتَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Hilkiya babban firist kuwa ya ce wa Shafan magatakarda, “Na iske littafin dokoki a cikin Haikalin Ubangiji.” Hilkiya kuwa ya ba Shafan littafin, shi kuwa ya karanta shi.