2 Kings 23:2 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai ya haura zuwa cikin haikalin Ubangiji tare da mutanen Yahuda, da na Urushalima, da firistoci, da annabawa, dukan mutane, manya da ƙanana. Ya karanta musu duk kalmomin Littafin Alkawari, wanda aka samu a haikalin Ubangiji.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَرْكِے كُوَ يَهَوْرَ ذُوَا غِدَنْ يَهْوٜىٰهْ ، تَرٜىٰدَ دُكَنْ مُتَنٜىٰنْ يَهُودَ دَ دُكَنْ مَذَوْنَنْ عُرُوشَلِيمَ؞ أَݣَويْ ڢِرِسْتُواْثِے دَ أَنَّبَاوَا دَ دُكَنْ مُتَنٜىٰ بَبَّ دَ ڧَرَمِ؞ سَيْ سَرْكِے يَكَرَنْتَ عَكُنّٜىٰنْسُ دُكَنْ كَلْمُواْمِنْ لِتَّڢِنْ يَرْجٜىٰجٜىٰنِيَ وَنْدَ عَكَ سَامُ أَ غِدَنْ يَهْوٜىٰهْ ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sa'an nan ya haura zuwa Haikalin Ubangiji tare da dukan jama'ar Yahuza, da dukan mazaunan Urushalima, da firistoci, da annabawa, da jama'a duka, ƙanana da manya. Sai ya karanta musu dukan maganar littafin alkawarin da aka iske a Haikalin Ubangiji.