2 Kings 23:30 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Bayin Yosiya suka ɗauko gawarsa daga Megiddo suka kai Urushalima, suka binne shi a kabarinsa. Sai mutanen ƙasar suka ɗauki Yehoyahaz ɗan Yosiya suka naɗa shi sarki a madadin mahaifinsa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ مَنْيَنْ سُواْجُواْجِنْ سَرْكِے يُواْسِيَا سُكَ طَوْكِ غَاوَرْ عَكٜىٰكٜىٰنْ دُواْكِنْ يَاڧِ دَغَ مٜىٰغِدُّواْ ذُوَا عُرُوشَلِيمَ عِنْدَ سُكَ بِنّٜىٰشِ عَكَبَرِنْسَ؞ مُتَنٜىٰنْ يَهُودَ سُكَ ذَاٻِ طَنْ سَرْكِے يُواْسِيَا مَيْ سُونَ يٜىٰهُواْوَهَظْ، سُكَ نَطَشِ سَرْكِے أَمَڟَيِنْ بَابَنْسَ؞ ﴿شٜىٰكَرَا 609 كَاڢِنْ حَيْڢُوَرْ عِيسَىٰ ﴾
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Fādawansa kuwa suka ɗauko gawarsa a karusa daga Magiddo, suka kawo Urushalima, suka binne a kabarinsa. Sai jama'ar ƙasa suka naɗa Yehowahaz ɗan Yosiya sarki a matsayin tsohonsa.