2 Kings 23:33 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Fir’auna Neko ya sa shi a sarƙa a Ribla a ƙasar Hamat don kada yă yi mulki a Urushalima, sa’an nan ya sa wa Yahuda harajin talenti ɗari na azurfa, da talenti ɗaya na zinariya.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
ڢِرْعَوْنَ نٜىٰكُواْ سَرْكِنْ مَصَرْ يَكَامَشِ يَكُلّٜىٰ أَغَرِنْ رِبْلَ عَڧَسَرْ هَمَتْ، دُواْمِنْ كَدَ يَيِ مُلْكِ أَ عُرُوشَلِيمَ؞ ڢِرْعَوْنَ نٜىٰكُواْ يَكُمَ سَا وَڧَسَرْ يَهُودَ هَرَاجِ نَكِلُواْ دُبُو عُكُ دَ طَرِے حُطُ نَأَظُرْڢَا دَ كِلُواْ تَلَاتِنْ دَ حُطُ نَظِينَارِيَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Fir'auna-neko ya sa shi a kurkuku a Ribla a ƙasar Hamat, don kada ya yi mulki a Urushalima. Ya kuma sa ƙasar ta riƙa ba da gandu, wato haraji, talanti ɗari na azurfa da talanti guda na zinariya.