2 Kings 25:11 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Nebuzaradan babban hafsan matsaran, ya kwashi waɗanda suka rage a cikin birnin, tare da sauran jama’a, da waɗanda suka miƙa kansu ga sarkin Babilon, ya kai su bauta.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ نٜىٰبُظَرَدَنْ شُوغَبَنْ یَنْ غَادِنْ سَرْكِے يَكَامَ سَوْرَنْ مُتَنٜىٰنْ دَ سُكَ رَغُ ثِكِنْ بِرْنِنْ عُرُوشَلِيمَ دَ سُواْجُواْجِ وَطَنْدَ سُكَ مِيڧَ كَنْسُ وُرِنْسَ دَ سَوْرَنْ مُتَنٜىٰنْ، دُكَنْسُ يَكَيْسُ بَوْتَا عَ بَابِيلَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai Nebuzaradan shugaban sojojin, ya kwashe sauran mutanen da suka ragu a birnin, da waɗanda suka gudu zuwa wurin Sarkin Babila, da sauran da suka ragu, ya kwashe ya kai su zaman talala.