2 Kings 3:27 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’an nan ya ɗauki ɗansa na fari, wanda zai gāje shi, ya yi hadaya da shi a bisa katangan birnin. Isra’ilawa suka firgita ƙwarai; sai suka janye suka koma ƙasarsu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَعَنً يَطَوْكِ طَنْ ڢَارِنْسَ وَنْدَ ذَيْ غَاجٜىٰشِ، يَمِيڧَ شِ هَدَايَ تَڧُواْنَاوَا عَكَنْ كَتَنْغَرْ بِرْنِنْ؞ سَبُواْدَ حَكَ، بَبَّنْ ڢُشِے يَتَاشِ عَكَنْ إِسْرَٰٓءِيلَاوَا، سَيْ سُكَ جَنْيٜىٰ سُكَ بَرْ بِرْنِنْ سُكَ كُواْمَ ڧَسَرْسُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai Sarkin Mowab ya kama babban ɗansa, wanda zai gāji sarautarsa, ya miƙa shi hadayar ƙonawa a kan garu. Isra'ilawa kuwa suka tsorata ko allahn abokan gāba zai cuce su, don haka suka janye, suka koma ƙasarsu.