2 Kings 4:8 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Wata rana Elisha ya tafi Shunem. Akwai wata mai arziki a can wadda ta gayyace shi cin abinci. Sai ya zama duk lokacin da yake wucewa, yakan tsaya a can don cin abinci.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
وَتَرَانَ أَلْيَسَعَ يَتَڢِے غَرِنْ شُنٜىٰمْ، عِنْدَ أَݣَويْ وَتَ مَثٜىٰ مَيْ أَرْزِڧِ؞ مَثٜىٰنْ تَنَاثٜىٰ مَسَ يَذُواْ يَثِ عَبِنْثِ أَغِدَنْتَ؞ تُنْدَغَ لُواْكَثِنْ، دُكْ سَعَدَّ يَكٜىٰ وُثٜىٰوَ تَوُرِنْ، سَيْ يَڟَيَ يَثِ عَبِنْثِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Wata rana Elisha ya wuce zuwa Shunem inda wata mace take da zama, sai ta gayyace shi cin abinci. Don haka duk lokacin da ya bi ta wannan hanya, sai ya ratsa ta gidanta, ya ci abinci.