2 Kings 5:17 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai Na’aman ya ce, “In ba za ka karɓa ba, ina roƙonka, bari a ba wa bawanka ƙasa gwargwadon abin da jakuna biyu za su iya ɗauka, gama bawanka ba zai sāke yin hadaya ta ƙonawa, ko wata hadaya ga wani allah ba, sai ga Ubangiji.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ نَعَمَنْ يَثٜىٰ «عِدَنْ بَذَاكَ كَرْٻَبَ، تُواْ، كَبَرْنِ إِنْ طِبَ غَارِنْ ڧَسَرْكُ وَنْدَ جَاكُنَنْ دُواْكِ بِيُ ذَاسُ عِيَ طَوْكَ عَكَيْ مِنِ غِدَا؞ غَمَا دَغَ يَنْذُ بَذَنْسَاكٜىٰ مِيڧَ هَدَايَ تَڧُواْنَاوَا كُواْ وَطَنْسُ هَدَايُ غَ وَنِ اللَّهْ بَ، سَيْدَيْ يَهْوٜىٰهْ ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Na'aman kuwa ya ce, “Da yake ka ƙi ka karɓa, ina roƙonka, ka ba baranka labtun alfadari biyu na ƙasa, gama nan gaba baranka ba zai ƙara miƙa hadaya ta ƙonawa ko baiko ga wani gunki ba, sai dai Ubangiji.