2 Kings 5:26 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Amma Elisha ya ce masa, “Ashe, ba ina tare da kai a ruhu ba sa’ad da mutumin ya sauko daga keken yaƙinsa ya tarye ka. Kana gani wannan lokaci ne da za a karɓi kuɗi, da riguna, da gonar inabi, da tumaki, da bijimai, da bayi maza da mata?
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عَمَّا أَلْيَسَعَ يَأَمْسَ يَثٜىٰمَسَ «أَيْ، إِنَ أَوُرِنْ ثِكِنْ رُوحُ سَعَدَّ مُتُمِنْ يَسَوْكَ دَغَ كٜىٰكٜىٰنْ دُواْكِنْسَ دُواْمِنْ يَسَدُ دَكَيْ؞ كَنَ غَنِ وَنَّنْ لُواْكَثِ نٜىٰ دَ ذَاعَ كَرْٻِ كُطِ دَ رِيغُنَ دَ غُواْنَرْ إِنَبِے دَ تُمَكِ دَ بِجِمَيْ دَ بَايِ مَظَا دَ مَاتَا؟
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Amma Elisha ya ce masa, “Ashe, ba ina tare da kai a ruhu ba, sa'ad da mutumin ya juyo daga karusarsa don ya tarye ka? Wannan shi ne lokacin karɓar kuɗi, da riguna, da gonaki na zaitun, da na inabi, da tumaki, da shanu, da barori mata da maza?