2 Kings 6:12 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai ɗaya daga cikin hafsoshinsa ya ce, “Babu waninmu, ranka yă daɗe; Elisha, annabin da yake a Isra’ila ne, yake faɗa wa sarkin Isra’ila dukan zancen da ka yi a ɗakinka.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ طَيَ دَغَ ثِكِنْسُ يَأَمْسَ يَثٜىٰ «رَنْكَيَدَطٜىٰ، بَابُوَنِ؞ أَيْ، أَنَّبِے أَلْيَسَعَ نَ إِسْرَٰٓءِيلَ نٜىٰ يَكٜىٰ ڢَطَا وَسَرْكِنْ إِسْرَٰٓءِيلَ دُكْ مَغَنَرْ دَ كَكٜىٰيِ، كُواْ أَطَاكِنْ ݣُونَنْكَ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ɗaya daga cikin fādawan ya ce, “A'a, ranka ya daɗe, sarki, ai, annabi Elisha ne wanda yake cikin Isra'ila, yake faɗa wa Sarkin Isra'ila maganar da kake faɗa a ɗakin kwananka.”