2 Kings 7:12 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai sarki ya tashi da daren nan ya ce wa hafsoshinsa, “Na san abin da Arameyawan suke shiri! Sun san game da yunwar da muke ciki a nan, domin haka sun bar sansaninsu suka shiga jeji suka ɓuya, suna nufin sa’ad da muka fita daga birni, sai su kama mu da rai, sa’an nan su shiga birnin.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ سَرْكِے يَتَاشِ دَ دَرٜىٰنْ، يَثٜىٰوَ مَاسُ يِمَسَ حِدِمَ «نَسَنْ أَبِنْدَ سُورِيَاوَنْ سُكٜىٰ شِرِ! سُنْسَنْ غَمٜىٰدَ يُنْوَرْ دَمُكٜىٰ عَثِكِ أَنَنْ، دُواْمِنْ حَكَ سُنْبَرْ سَنْسَنِنْسُ سُكَ شِغَ دَاجِ سُكَ ٻُيَ؞ سُنَ تُنَانِ ثٜىٰوَ عِدَنْ مُنْ بَرْ بِرْنِ مُكَ ڢِتَ نٜىٰمَنْ عَبِنْثِ، سَيْ سُڢَاطُواْ مَنَ، سُكَكَّامَمُ دَرَيْ، سُڨُوثٜىٰ بِرْنِنْمُ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai sarki ya tashi da dare ya ce wa fādawansa, “Bari in faɗa muku irin shirin da Suriyawa suka yi a kanmu. Sun sani muna fama da yunwa, domin haka suka fita daga sansanin suka ɓuya a karkara, suna nufin sa'ad da muka fita daga birnin, sai su kama mu da rai, sa'an nan su shiga birnin.”