2 Kings 8:1 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
To, Elisha ya riga ya ce wa matan da ya tā da ɗanta daga matattu, “Ki kwashe iyalinki ku tafi duk inda za ku tafi na ɗan lokaci, domin Ubangiji ya sa a yi yunwa na shekara bakwai a ƙasar.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دَا مَا أَلْيَسَعَ يَڢَطَا وَمَثٜىٰنْدَ يَمَيْدَ رَنْ طَنْتَ دَغَ مَتَتُّو ثٜىٰوَ تَتَاشِ دَ عِيَلِنْتَ سُغُدُ ذُوَا وَنِ وُرِے، غَمَا يَهْوٜىٰهْ يَثٜىٰ ذَيْ عَيْكَ دَ يُنْوَ عَڧَسَرْ حَرْ شٜىٰكَرَا بَݣَويْ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Elisha kuwa ya ce wa matar da ya ta da ɗanta daga matattu, “Ki tashi, ke da gidanki, ki zauna duk inda kika samu, gama Ubangiji ya sa a yi yunwa a ƙasar har shekara bakwai.”