2 Samuel 1:21 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Ya duwatsun Gilbowa, kada a sāke yin ruwa ko raɓa a kanku, balle gonakin da suke ba da hatsin hadaya su ƙara bayarwa. Gama a can ne garkuwoyin manyan sojoji suka kwanta, suka kwanta a wulaƙance. Garkuwar Shawulu kuwa, ba za a ƙara shafa mata mai ba.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
«يَا كُو مَنْيَنْ تُدَّنْ غِلْبُواْوَ، كَدَ أَ سَاكٜىٰيِنْ ضُوَ كُواْ رَٻَ عَكَنْكُ، كَدَ غُواْنَكِنْكُ سُڢِتَرْدَ حَڟِ؞ غَمَا عَثَنْ نٜىٰ غَرْكُوُاْيِنْ مَنْيَنْ سُواْجُواْجِ سُكَ ݣُونْتَ، سُكَ ݣُونْتَ أَوُلَڧَنْثٜىٰ؞ غَرْكُوَرْ طَالُوتَ كُوَ، بَذَاعَ ڧَارَ شَاڢَ مَتَ مَيْبَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“Kada ruwan sama ko raɓa su zubo kan tuddan Gilbowa. Da ma gonakinta su zama marasa ba da amfani. Gama a can ne aka zube garkuwoyin jarumawa a wulakance, Tsatsa ta rufe garkuwar Saul.