2 Samuel 10:8 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ammonawa suka fita suka ja dāgār yaƙi a ƙofar shiga birninsu, yayinda Aram-Zoba, da na Rehob, da mutane Tob, da kuma na Ma’aka, suka ja tasu dāgār a karkara.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ أَمُّواْنَاوَا سُكَ ڢِتَ سُكَيِ شِرِ دُواْمِنْ يَاڧِ عَڧُواْڢَرْ رَبَّهْ بَبَّنْ بِرْنِنْسُ؞ عَمَّا مُتَنٜىٰنْ سُورِيَ دَغَ ذُوابَ دَ رٜىٰهُوابْ دَ سُواْجُواْجِ دَغَ تُوابْ دَ مَعَكَ سُكَيِ شِرِنْ يَاڧِنْسُ أَ ڢِيلِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ammonawa suka fita suka ja dāgar yaƙi a ƙofar garin, amma Suriyawan Zoba da na Rehob, da mutanen Ish-tobi da na Ma'aka suka ja tasu dāgar a karkara.