2 Samuel 11:17 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’ad da mutanen garin suka fito suka yaƙi Yowab, sai waɗansu mutane daga sojojin Dawuda suka mutu; Uriya mutumin Hitti ma ya mutu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سُواْجُواْجِنْ بِرْنِنْ سُكَ ڢِتَ سُكَ ڢَاطَوَ يُواْوَبْ دَ يَاڧِ، عَكَ كَشٜىٰ وَطَنْسُ سُواْجُواْجِنْ دَاوُدَ؞ عُرِيَ مُتُمِنْ هِتِّ كُوَ يَنَ ثِكِنْ وَطَنْدَ عَكَ كَشٜىٰ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Mutanen garin suka fito suka yi yaƙi da Yowab. Suka kashe waɗansu daga cikin sojojin Dawuda. Uriya Bahitte, shi ma aka kashe shi.