2 Samuel 11:25 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Dawuda ya ce wa manzon, “Ka gaya wa Yowab, ‘Kada ka bar wannan yă dame ka; yadda takobi ya lamushe wannan, haka zai lamushe wancan ma. Ku ƙara matsa wa garin lamba, ku hallaka shi.’ Ka faɗa haka don ka ƙarfafa Yowab.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دَاوُدَ يَثٜىٰ وَطَنْ عَيْكَنْ «كَكُواْمَ كَڧَرْڢَڢَ يُواْوَبْ؞ كَثٜىٰمَسَ كَدَ يَدَامُ غَمٜىٰدَ أَبِنْدَ يَڢَرُ، غَمَا تَكُواْبِے بَايَ ذَاٻٜىٰنْ وَنْدَ ذَيْ كَشٜىٰ؞ كَڢَطَا مَسَ ثٜىٰوَ يَڧَارَ مَڟَا وَغَرِنْ لَمْبَ حَرْ سَيْ أَنْرُشٜىٰشِ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Dawuda ya ce wa manzon, “Je ka ka faɗa wa Yowab kada wannan abu ya dame shi, ai, takobi ba ya tarar wanda zai kashe. Ku ƙara matsa wa garin lamba, ku faɗa masa har ku ragargaza shi. Ka ƙarfafa Yowab.”