2 Samuel 12:20 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’an nan Dawuda ya tashi daga ƙasa. Bayan ya yi wanka, ya shafa mai, ya kuma canja rigunarsa, sa’an nan ya shiga gidan Ubangiji ya yi sujada. Sai ya tafi gidansa, ya nemi a ba shi abinci, aka ba shi, ya kuwa ci.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَعَنً دَاوُدَ يَتَاشِ دَغَ ڧَسَا؞ بَايَنْدَ يَيِ وَنْكَ، يَشَاڢَ مَيْ، يَثَنْجَ رِيغُنَنْسَ؞ سَيْ يَتَڢِے غِدَنْ يَهْوٜىٰهْ يَيِ سُجَّدَ؞ سَعَنً يَكُواْمَ غِدَا، يَثٜىٰ عَبَاشِ عَبِنْثِ يَكُمَثِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai Dawuda ya tashi daga ƙasa, ya yi wanka, ya shafa mai, ya sake tufafinsa, ya tafi ɗakin sujada, ya yi sujada, sa'an nan ya koma gidansa ya ce a kawo abinci. Suka kawo masa abinci ya ci.