2 Samuel 12:9 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Me ya sa ka rena maganar Ubangiji ta wurin yin mugunta haka a idonsa? Ka kashe Uriya mutumin Hitti da takobi, ka kuma ɗauki matarsa tă zama matarka. Ka kashe shi da takobin Ammonawa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دُوانْمٜىٰ كَرٜىٰنَ عُمَرْنِنْ يَهْوٜىٰهْ حَرْ كَعَيْكَتَ أَبِنْدَ يَكٜىٰمُوغُ أَعِدُوانْسَ؟ كَبُغِ عُرِيَ مُتُمِنْ هِتِّ دَ تَكُواْبِے؞ كَكَشٜىٰشِ دَ تَكُواْبِنْ أَمُّواْنَاوَا، كَكُمَ طَوْكِ مَاتَرْسَ تَذَمَ تَاكَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Me ya sa ka raina maganar Ubangiji, har da ka aikata mugun abu haka a gabansa? Ka kashe Uriya Bahitte ta hannun Ammonawa, ka ɗauki matarsa ta zama matarka.