2 Samuel 13:20 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Absalom ɗan’uwanta ya ce mata, “Amnon, ɗan’uwanki ya ɓata ki ko? To, ki yi shiru ’yar’uwata; ai, ɗan’uwanki ne. Kada wannan abu yă dame ki.” Tamar kuwa ta zauna a gidan ɗan’uwanta Absalom, zaman kaɗaici.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دَ أَبْسَلُوامْ طَنْعُوَنْتَ يَغَنْتَ سَيْ يَتَمْبَيٜىٰتَ يَثٜىٰ «أَمْنُوانْ نٜىٰ يَݣُونَ دَكٜىٰ؟ يَنْذُ سَيْ كِيِ شِضُ، یَرْعُوَتَ؞ أَيْ، شِے طَنْعُوَنْكِ نٜىٰ؞ كَدَ كِيَرْدَ وَنَّنْ يَٻَاتَ مِكِ ذُوثِيَا سُواْسَيْ؞» تَمَرْ كُوَ تَذَوْنَ أَغِدَنْ طَنْعُوَنْتَ أَبْسَلُوامْ، تَنَ ڢِدَّ ذُوثِيَا غَمٜىٰدَ رَايُوَا؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Absalom wanta ya tambaye ta, ya ce, “Ko Amnon wanki ya ɓata ki? To, yi shiru, ƙanwata, shi wanki ne, kada ki damu da yawa.” Tamar kuwa ta zauna a kaɗaice a gidan Absalom wanta.