2 Samuel 13:28 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Absalom ya umarci mutanensa ya ce, “Ku saurara! Sa’ad da Amnon ya bugu sosai da giya na kuma ce muku, ‘Ku bugi Amnon,’ sai ku kashe shi. Kada ku ji tsoro. Ashe, ba ni ne na ba ku wannan umarni ba? Ku yi ƙarfin hali, ku kuma yi jaruntaka.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ أَبْسَلُوامْ يَعُمَرْثِ مَاسُ يِمَسَ حِدِمَ يَثٜىٰ «كُلُورَ، أَ لُواْكَثِنْ دَ أَمْنُوانْ يَكٜىٰ جِنْ دَاطِنْ ضُوً إِنَبِے، سَعَدَّ نَثٜىٰ مُكُ كُبُغِ أَمْنُوانْ، سَيْ كُكَشٜىٰشِ؞ كَدَ كُجِڟُواْرُواْ غَمَا نِنٜىٰ نَا عُمَرْثٜىٰكُ؞ كُيِ ڧَرْڢِنْ ذُوثِيَا بَابُوَسَ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Absalom ya umarci barorinsa, ya ce, “Ku lura sa'ad da Amnon ya bugu da ruwan inabi, in na ce, ‘Bugi Amnon’, sai ku kashe shi. Kada ku ji tsoro, gama ni na umarce ku, sai dai ku yi ƙarfin hali, ku yi jaruntaka.”