2 Samuel 13:32 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Amma Yonadab, ɗan Shimeya ɗan’uwan Dawuda ya ce, “Kada ranka yă daɗe yă yi tunani cewa an kashe dukan ’ya’yan sarki maza; Amnon ne kaɗai ya mutu. Wannan ce niyyar Absalom tun lokacin da Amnon ya yi wa Tamar ’yar’uwansa fyaɗe.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عَمَّا يُواْنَدَبْ طَنْ شِمٜىٰيَ طَنْعُوَنْ دَاوُدَ يَثٜىٰ وَ دَاوُدَ «رَنْكَيَدَطٜىٰ! كَدَ كَطَوْكَ أَنْكَشٜىٰ دُكَنْ یَیَ مَذَنْكَ؞ أَمْنُوانْ نٜىٰ كَطَيْ عَكَ كَشٜىٰ؞ أَبْسَلُوامْ يَشِرْيَ حَكَ تُنْ رَانَرْ دَ أَمْنُوانْ يَتِلَسْتَ یَرْعُوَرْسَ تَمَرْ تَݣُونَ دَشِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Amma Yonadab, ɗan Shimeya, ɗan'uwan Dawuda, ya ce, “Ranka ya daɗe, ba fa dukan 'ya'yan sarki aka kashe ba. Amnon ne kaɗai aka kashe ta umarnin Absalom, gama ya ƙudura wannan tun daga ranar da Amnon ya yi wa Tamar ƙanwarsa faɗe.