2 Samuel 14:2 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Saboda haka Yowab ya aiki wani zuwa Tekowa, ya sa a zo da wata mace mai hikima. Ya ce mata, “Ki yi kamar kina makoki. Ki sa rigar makoki, kada kuwa ki shafa mai. Ki yi kamar macen da ta yi kwanaki da yawa, tana makokin matattu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ يُواْوَبْ يَعَيْكَ وَنِ ذُوَا غَرِنْ تٜىٰكُواْوَ، عَكَٰوُاْ مَسَ وَتَ مَثٜىٰ مَيْ حِكِمَ؞ دَتَذُواْ سَيْ يُواْوَبْ يَثٜىٰ مَتَ «كِيِ كَمَرْ كِنَ بَڧِنْ ثِكِ؞ كِسَا رِيغُنَنْ نُونَ بَڧِنْ ثِكِ، كَدَ كُمَ كِشَاڢَ مَيْ؞ كِيِ كَمَرْ مَثٜىٰنْ دَ تَيِ ݣُونَكِے تَنَ بَڧِنْ ثِكِنْ مُتُوَرْ وَنِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
sai ya aika zuwa Tekowa a kira masa wata mace mai hikima. Da ta zo, ya ce mata, “Ki yi kamar kina makoki, ki sa rigunan makoki, kada ki shafa mai. Ki yi kamar wadda ta yi kwanaki da yawa tana makokin rasuwar wani.