2 Samuel 14:32 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Absalom ya ce wa Yowab, “Kai, na aika, ‘Ka zo nan don in aike ka wurin sarki ka tambaya, “Me ya sa na dawo daga Geshur? Ai, ya fi mini a ce ina can har yanzu!” ’ Yanzu kuwa, ina so in ga sarki, kuma idan na yi wani laifi, to, yă kashe ni.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
أَبْسَلُوامْ يَأَمْسَ مَسَ يَثٜىٰ «دُواْمِنْ كَاڧِ ذُوَا سَعَدَّ نَعَيْكَ عَكِرَاكَ؞ نَسُواْ إِنْ عَيْكٜىٰكَ وُرِنْ سَرْكِے كَتَمْبَيَ مِنِ دَلِيلِنْدَ يَدَاوُاْ دَنِے دَغَ غٜىٰشُرْ؞ أَيْ، يَڢِ مِنِ إِنْذَوْنَ عَثَنْ! يَنْذُ إِنَ سُواْ إِنْغَا سَرْكِے، عِدَنْ نَيِمَسَ لَيْڢِے تُواْ، سَيْ يَكَشٜىٰنِ!»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Absalom ya ce wa Yowab, “Har sau biyu na aika maka domin ka zo in aike ka wurin sarki, ka tambaya mini, ‘Ko me ya sa na komo daga Geshur?’ Da ma ina can har yanzu, ai, da ya fi mini. Yanzu har ni in tafi wurin sarki, idan ina da laifi, to, ya kashe ni.”