2 Samuel 14:7 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
To, ga duk iyali sun hau kan baiwarka, suna cewa, ‘Ki ba mu ɗayan da ya kashe ɗan’uwansa mu kashe don ran ɗan’uwansa da ya kashe; sa’an nan za mu hallaka magājin shi ma.’ Za su kashe garwashin wuta mai ci da nake da shi kaɗai, su bar mijina ba suna, ba jika, a duniya.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
تُواْ، عَيَنْظُ حَكَ، دُكَنْ دَنْ‌غِ سُنْتَاسُواْ مِنِ دَ ذَاڢِ ثٜىٰوَ إِنْمِيڧَ مُسُ وَنْدَ يَكَشٜىٰ طَنْعُوَنْسَ، دُواْمِنْ سُكَشٜىٰشِ سَبُواْدَ رَنْ طَنْعُوَنْسَ وَنْدَ يَكَشٜىٰ، كُواْ دَمَا ذَاسُكَشٜىٰ وَنْدَ ذَيْثِ غَادُوانْ نٜىٰ؞ طَانَ كَمَرْ طَنْ ضَغُواْوَرْ هَرْشٜىٰنْ وُتَاتَ نٜىٰ، عِدَنْ سُنْ كَشٜىٰشِ ذَاعَ بَرْ نِے بَابُ كُواْمٜىٰ؞ سَعَنً سُونَنْ مِجِنَ دَ نَظُرِيَرْسَ ذَيْ ٻَثٜىٰ دَغَ دُونِيَا؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Yanzu kuwa dukan dangi sun tasar mini, suna cewa, in ba da ɗayan wanda ya kashe ɗan'uwansa domin su kashe shi saboda ran ɗan'uwansa da ya kashe. Wato za su hallaka magāji ke nan, ta haka za a yi biyu babu ke nan, su bar mijina ba suna ko zuriya a duniya.”