2 Samuel 15:12 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Yayinda Absalom yake miƙa hadaya, ya aika a kira Ahitofel mutumin Gilo, mai ba wa Dawuda shawara, yă zo daga Gilo garinsa. Ta haka makircin ya ƙara ƙarfi, masu bin Absalom kuma suka yi ta ƙaruwa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
أَ لُواْكَثِنْ دَ أَبْسَلُوامْ ذَيْ مِيڧَ هَدَايَ، يَعَيْكَ ذُوَا غَرِنْ غِلُواْ عَكَٰوُاْ مَسَ أَهِتُواْڢٜىٰلْ مُتُمِنْ غِلُواْ، وَنْدَ يَكٜىٰبَا سَرْكِے دَاوُدَ شَوَرَا؞ تَهَكَ وَنَّنْ شِرِنْ تَاوَيٜىٰ يَيِ ڧَرْڢِے، مَاسُ غُواْيُوانْ بَايَنْ أَبْسَلُوامْ سُكَيِ تَڧَارَ يَوَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Lokacin da Absalom yake miƙa hadaya, sai ya aika zuwa Gilo a kira masa Ahitofel Bagilone mai ba Dawuda shawara. Maƙarƙashiyar kuwa ta yi ƙarfi. Mutane masu haɗa kai da Absalom suka riƙa ƙaruwa kullum.