2 Samuel 15:25 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’an nan sarki ya ce wa Zadok, “Ka komar da akwatin alkawarin Allah cikin birnin. Idan na sami tagomashi a idon Ubangiji, zai dawo da ni, yă kuma sa in sāke gan shi a mazauninsa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عَمَّا سَرْكِے يَثٜىٰ وَ ظَدُواكْ «كَكُواْمَرْدَ عَݣُوتِنْ يَرْجٜىٰجٜىٰنِيَ نَ اللَّهْ ثِكِنْ بِرْنِنْ؞ عِدَنْ نَسَامِ ڢَضٍ جِنِ أَعِدُوانْ يَهْوٜىٰهْ ، ذَيْكُواْمُواْ دَنِے إِنْ سَاكٜىٰ غَنِنْ عَݣُوتِنْ يَرْجٜىٰجٜىٰنِيَ دَ كُمَ وُرِنْ ذَمَنْسَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sa'an nan sarki ya ce wa Zadok, “Ka koma da akwatin alkawarin Allah cikin birnin. Idan na sami tagomashi a wurin Ubangiji zai komo da ni, zan sāke ganin akwatin da mazaunin zatinsa.