2 Samuel 15:6 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Absalom ya yi ta yin haka ga dukan Isra’ilawan da suka zo wurin sarki don neman adalci, ta haka kuwa ya saci zukatan mutanen Isra’ila.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
أَبْسَلُوامْ يَيِ تَيِنْ حَكَ غَ كُواْوَنٜىٰ مُتُمِنْ إِسْرَٰٓءِيلَ وَنْدَ يَذُواْ وَجٜىٰنْ سَرْكِے دَاوُدَ دُواْمِنْ شَرِيعَ؞ تَهَكَ يَسَاثِ ظُكَاتَنْ مُتَنٜىٰنْ إِسْرَٰٓءِيلَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Haka Absalom ya riƙa yi wa dukan Isra'ilawan da suka zo wurin sarki don shari'a. Da haka ya saci zukatan mutanen Isra'ila.