2 Samuel 18:33 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai gaban sarki ya faɗi. Ya haura zuwa ɗakin da yake kan katangar hanyar shiga ya yi kuka. Yayinda yake tafiya ya ce, “Ya ɗana Absalom! Ɗana, ɗana Absalom! Da ma a ce ni ne na mutu maimakonka. Ya Absalom, ɗana, ɗana!”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ ذُوثِيَارْ سَرْكِے تَڟِنْكٜىٰ، يَهَوْ ثِكِنْ وَنِ طَاكِنْ دَيَكٜىٰ عَبِسَ طَاكِنْ تَارُواْ ثِكِنْ ڧُواْڢَرْ بِرْنِ يَنَ تَ كُوكَا؞ يَيِ كُوكَا يَنَ ثٜىٰوَ «أَيَّ، طَانَ أَبْسَلُوامْ! طَانَ! أَيَّ، طَانَ أَبْسَلُوامْ! دَمَا نِنٜىٰ نَمُتُ، بَكَيْبَ! أَيَّ، أَبْسَلُوامْ طَانَ، طَانَ!»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai zuciyar sarki ta tsinke, ya hau cikin ɗakin da yake kan garun ƙofar garin yana ta kuka, yana cewa, “Ya ɗana Absalom, ɗana! Wayyo, ɗana Absalom! Da ma ni ne na mutu, ba kai ba. Ya Absalom, ɗana, ɗana!”