2 Samuel 20:1 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Akwai wani mai tā-da-na-zaune-tsaye, sunansa Sheba, ɗan Bikri, daga kabilar Benyamin, a wurin. Sai ya busa ƙaho, ya yi ihu ya ce, “Ba mu da rabo a wurin Dawuda, ba mu da sashe a wurin ɗan Yesse! Kowa yă nufi tentinsa, ya Isra’ila!”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
أَوُرِنْ كُوَ أَݣَويْ وَنِ طَنْ إِسْكَ مَيْ سُونَ شٜىٰبَ طَنْ بِكِرِ دَغَ ذُرِيَرْ بِلِيَامِنُ؞ يَبُوسَ ڧَهُواْ يَتَادَ مُرْيَ يَثٜىٰ، «إِنَا ضُوَنْمُ دَ دَاوُدَ! أَيْ، بَامُ دَ غَادُواْ أَوُرِنْ طَنْ يٜىٰسّٜىٰ! يَا إِسْرَٰٓءِيلَ، كُواْوَ يَكُواْمَ تٜىٰنْتِنْسَ!»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Da can akwai wani mutumin banza, ana ce da shi Sheba, ɗan Bikri, daga kabilar Biliyaminu. Shi kuwa ya busa ƙaho, ya ce, “Ba mu da rabo a wurin Dawuda, ba mu kuwa da gado wurin ɗan Yesse. Ya Isra'ilawa, kowa ya gudu zuwa alfarwarsa.”