2 Samuel 23:1 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Waɗannan su ne kalmomin Dawuda na ƙarshe. “Abubuwan da Dawuda ɗan Yesse ya yi magana a kai, abubuwan da mutumin da Mafi Ɗaukaka ya girmama. Mutumin da Allah na Yaƙub ya zaɓa yă zama sarki, wanda kuma yake mawaƙi waƙoƙin Isra’ila.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
وَنَّنْ عِتَثٜىٰ مَغَنَرْ دَاوُدَ تَڧَرْشٜىٰ؞ كَلْمُواْمِنْ دَاوُدَ طَنْ يٜىٰسّٜىٰ، كَلْمُواْمِنْ مُتُمِنْ دَ اللَّهْ يَطَوْكَكَ، مُتُمِنْ دَ اللَّهْ نَ يَعْڧُوبَ يَكٜىٰٻٜىٰ سَرْكِے، مُتُمِنْ إِسْرَٰٓءِيلَ مَيْ رٜىٰرَ وَاڧُواْڧِ مَاسُ دَاطِے؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Wannan ita ce maganar Dawuda ta ƙarshe. Dawuda ɗan Yesse, shi ne mutumin da Allah ya ɗaukaka, wanda Allah na Yakubu ya zaɓa ya zama sarki, wanda kuma ya shirya waƙoƙin Isra'ila. Dawuda ya ce,