2 Samuel 23:13 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
A lokacin girbi, uku daga cikin shugabanni talatin suka gangaro zuwa wurin Dawuda a kogon Adullam. A lokacin kuwa sojojin Filistiyawa sun kafa sansani a Kwarin Refayim.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
وَتَرَانَ أَ لُواْكَثِنْ غِرْبِے، عُكُ دَغَ ثِكِنْ مَنْيَنْ سُواْجُواْجِ تَلَاتِنْ نَ دَاوُدَ سُكَذُواْ وُرِنْسَ أَ كُواْغُوانْ أَدُلَّمْ؞ ڧُنْغِيَرْ سُواْجُواْجِنْ ڢِلِسْتِيَاوَا كُوَ سُكَ كَڢَ سَنْسَنِنْ يَاڧِنْسُ أَ ݣُورِنْ رٜىٰڢَيَاوَا؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai jarumawa uku daga cikin jarumawa talatin, suka tafi wurin Dawuda a kogon Adullam, gab da lokacin girbi. A lokacin kuwa Filistiyawa sun kafa sansani a kwarin Refayawa.