2 Samuel 24:10 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Bayan Dawuda ya ƙidaya mayaƙan, lamirinsa ya kāshe shi, sai ya ce wa Ubangiji, “Ya Ubangiji na yi laifi ƙwarai a kan abin da na yi. Ina roƙonka ka gafarta wa bawanka. Na yi wauta ƙwarai.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عَمَّا بَايَنْدَ دَاوُدَ يَغَمَ ڧِرْغَرْ، سَيْ ذُوثِيَارْسَ تَدَامٜىٰشِ؞ سَيْيَثٜىٰ وَ يَهْوٜىٰهْ «نَايِ مَكَ ذُنُوبِ ڨُورَيْ تَدَلِيلِنْ وَنَّنْ ڧِرْغَ! إِنَ ضُواْڧُوانْكَ، يَا يَهْوٜىٰهْ ، كَغَاڢَرْتَا مِنِ، غَمَا نَايِ وَوَنْثِ سُواْسَيْ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Bayan da Dawuda ya ƙidaya mutane, sai lamirinsa ya kā da shi, ya ce wa Ubangiji, “Na yi laifi ƙwarai a kan abin da na yi. Ina roƙonka, ya Ubangiji, ka gafarta mini, gama na yi wauta.”