2 Samuel 6:2 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Shi, da dukan mutanensa suka tashi daga Ba’ala-Yahuda don su hauro da akwatin alkawarin Allah, wanda ake kira da Sunan Ubangiji Maɗaukaki, wanda yake zama a tsakanin kerubobin da suke a kan akwatin alkawarin.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ دَاوُدَ يَتَاشِ دَغَ بَعَلٜىٰ عَيَنْكِنْ يَهُودَ، وَتُواْ كِرِيَتْ يٜىٰيَرِمْ، يَتَڢِے دَ دُكَنْ مُتَنٜىٰنْ دَسُكٜىٰ تَرٜىٰ دَشِ دُواْمِنْ سُكَٰوُاْ عَݣُوتِنْ يَرْجٜىٰجٜىٰنِيَ نَ اللَّهْ ؞ أَغَبَنْ عَݣُوتِنْ كُوَ عَكَنْ كِرَا غَ سُونَنْ يَهْوٜىٰهْ مَڢِے غِرْمَ، سَرْكِے مَيْ ذَمَ عَبِسَ حَلِتُّو مَاسُ ڢِكَڢِكَيْ وَطَنْدَ سُكٜىٰ عَكَنْ مُرْڢِنْ عَݣُوتِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai ya tafi tare da su duka zuwa Kiriyat-yeyarim domin ya kawo akwatin Alkawarin Allah, wanda ake kira da sunan Ubangiji Mai Runduna wanda yake zaune a tsakanin kerubobin.