2 Samuel 6:20 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Da Dawuda ya koma gida don yă sa wa gidansa albarka, sai Mikal ’yar Shawulu ta fito don tă tarye shi, sai ta ce, “Tabbas sarkin Isra’ila ya fiffita kansa yau, ya tuɓe a gaban bayinsa ’yan mata, kamar yadda duk marar kunya yakan yi!”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دَ دَاوُدَ يَكُواْمَ غِدَا دُواْمِنْ يَ أَلْبَرْكَثِ غِدَنْسَ، سَيْ مِكَلْ مَاتَرْ دَاوُدَ وَدَّ تَكٜىٰ یَرْ طَالُوتَ تَڢِتَ تَتَرْيٜىٰشِ؞ تَا ثٜىٰمَسَ «لَلَّيْ سَرْكِنْ إِسْرَٰٓءِيلَ يَيِ بَبَّنْ أَبُ يَوْ! يَبُوطٜىٰ جِكِنْسَ أَغَبَنْ یَنْ مَاتَانْدَ سُكٜىٰ بَايِنْسَ، كَمَرْ يَدَّ مُتُمِنْ بَنْظَ مَرَرْ كُنْيَا يَكٜىٰ بُوطٜىٰ جِكِنْسَ!»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Da Dawuda ya komo gida domin ya sa wa iyalinsa albarka, Mikal, 'yar Saul, ta fito domin ta tarye shi, ta ce masa, “Ƙaƙa Sarkin Isra'ila ya ɗauki kansa yau? Ya kware darajarsa a gaban barorinsa mata kamar yadda shakiyyai suke yi.”