2 Samuel 8:6 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ya ajiye ƙungiyoyi sojoji a masarautar Arameyawan Damaskus, Arameyawa kuwa suka zama bayinsa, suka biya shi haraji. Ubangiji ya ba Dawuda nasara a duk inda ya tafi.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ يَكَڢَ بَرِكُواْكِنْ سُواْجُواْجِنْسَ أَ دِمَشْڧُ تَ سُورِيَ؞ مُتَنٜىٰنْ سُورِيَ كُوَ سُكَ ذَمَ بَايِنْ دَاوُدَ سُنَ كَٰوُاْ مَسَ هَرَاجِ؞ يَهْوٜىٰهْ يَكَنْبَا دَاوُدَ نَصَرَا دُكْ وُرِنْدَ يَتَڢِے؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sa'an nan ya ajiye ƙungiyoyin sojojinsa a Suriya ta Dimashƙu. Suriyawa suka zama talakawan Dawuda, suka riƙa kawo masa haraji. Duk inda Dawuda ya tafi, Ubangiji yakan taimake shi.