2 Samuel 9:6 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’ad da Mefiboshet ɗan Yonatan, ɗan Shawulu, ya zo wurin Dawuda, sai ya rusuna har ƙasa ya yi gaisuwar bangirma. Dawuda ya ce, “Mefiboshet!” Shi kuwa ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, ga ni, bawanka.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دَ مٜىٰڢِبُواْشٜىٰتْ طَنْ يُواْنَتَنْ، جِيكَنْ طَالُوتَ يَذُواْ غَبَنْ دَاوُدَ، سَيْ يَرُسُنَ حَرْ ڧَسَا يَيِ غَيْسُوَا؞ دَاوُدَ يَثٜىٰ مَسَ «مٜىٰڢِبُواْشٜىٰتْ!» سَيْ مٜىٰڢِبُواْشٜىٰتْ يَأَمْسَ «رَنْكَيَدَطٜىٰ، غَا بَاوَنْكَ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Da aka zo da Mefiboshet, ɗan Jonatan, wato jikan Saul, sai ya rusuna har ƙasa, ya yi gaisuwa. Dawuda ya ce, “Mefiboshet!” Ya amsa, “Ranka ya daɗe, ga baranka.”