Acts 14:15 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Ya ku mutane, don me kuke yin haka? Ai, mu ma mutane ne kawai, ’yan adam ne kamar ku. Mun kawo muku labari mai daɗi ne, muna gaya muku ku juya daga waɗannan abubuwa banza, ku juyo ga Allah mai rai, wanda ya yi sama da ƙasa da teku da kuma dukan abin da yake cikinsu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
«دُوانْمٜىٰ كُكٜىٰيِنْ حَكَ؟ أَيْ، مُو مَا مُتَنٜىٰنٜىٰ كَمَرْكُ، مُنْ دَيْ كَٰوُاْ مُكُ لَابَرِ مَيْ دَاطِے نٜىٰ، دُواْمِنْ كُجُويَا وَ أَبُبُوَنْ بَنْظَنَّنْ بَايَ، كُكُمَ جُويُواْ غَ اللَّهْ مَيْ رَيْ، وَنْدَ يَحَلِثِّ سَمَ دَ ڧَسَا دَ تٜىٰكُ دَ كُمَ دُكَنْ أَبِنْدَ يَكٜىٰ ثِكِنْسُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“Don me kuke haka? Ai, mu ma 'yan adam ne kamarku, mun dai kawo muku bishara ne, domin ku juya wa abubuwan banzan nan baya, ku juyo ga Allah Rayayye, wanda ya halicci sama, da ƙasa, teku, da kuma dukkan abin da yake a cikinsu.