Acts 15:2 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Wannan ya kai Bulus da Barnabas suka shiga babban gardama da muhawwara da su. Saboda haka aka naɗa Bulus da Barnabas tare da waɗansu masu bi, su haura zuwa Urushalima don su ga manzanni da dattawa a kan wannan magana.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
بَا ڧَرَمَرْ غَرْدَمَ بُلُسْ دَ بَرْنَبَ سُكَيِ دَ مُتَنٜىٰنَّنْ عَكَنْ وَنَّنْ مَغَنَبَ؞ سَيْ عَكَسَا بُلُسْ دَ بَرْنَبَ دَ كُمَ وَطَنْسُ سُجٜىٰ عُرُوشَلِيمَ وُرِنْ مَنْذَنِّے دَ دَتَّاوَنْ جَمَعَرْ مَاسُبِے دُواْمِنْ سُتَتَّوْنَ عَكَنْ وَنَّنْ مَغَنَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
A kan wannan magana kuwa ba ƙaramar gardama da muhawwara Bulus da Barnaba suka sha yi da mutanen ba. Sai aka sa Bulus da Barnaba da kuma waɗansunsu, su je Urushalima gun manzanni da dattawan Ikkilisiya a kan wannan magana.