Acts 15:22 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai manzanni da dattawa, tare da dukan ikkilisiya, suka yanke shawara su zaɓi waɗansu daga cikin mutanensu su kuma aike su zuwa Antiyok tare da Bulus da Barnabas. Sai suka zaɓi Yahuda (wanda ake kira Barsabbas) da kuma Sila, mutum biyu da suke shugabanni cikin ’yan’uwa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ مَنْذَنِّےنْ دَ دَتَّاوَنْ جَمَعَرْ مَاسُبِے، تَرٜىٰدَ دُكَنْ یَنْ جَمَعَرْ مَاسُبِے، سُكَغَ يَيِݣَوْ سُذَاٻِ وَطَنْسُ دَغَ ثِكِنْسُ، سُأَيْكٜىٰسُ ذُوَا أَنْتَكِيَ تَرٜىٰدَ بُلُسْ دَ بَرْنَبَ؞ سَيْ سُكَ ذَاٻِ يَهُودَ، وَنْدَ عَكٜىٰثٜىٰ دَشِ بَرْسَبَ دَ كُمَ سِيلَ، وَطَنْدَ سُو شُوغَبَنِّنٜىٰ ثِكِنْ مَاسُبِے؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai manzanni da dattawan Ikkilisiya, tare da dukan 'yan Ikkilisiya, suka ga ya kyautu su zaɓi waɗansu daga cikinsu, su aike su Antakiya tare da Bulus da Barnaba. Sai suka aiki Yahuza, wanda ake kira Barsaba, da kuma Sila, shugabanni ne cikin 'yan'uwa,