Acts 16:1 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Bulus ya kai Derbe sa’an nan kuma zuwa Listira, inda wani almajiri mai suna Timoti yake da zama, wanda mahaifiyarsa mutuniyar Yahuda ce kuma mai bi ce, amma mahaifinsa mutumin Hellenawa ne.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ بُلُسْ يَجٜىٰ دَرْبٜىٰ دَ لِسْتِرَ؞ أَݣَويْ وَنِ أَلْمَجِرِ أَ لِسْتِرَ مَيْ سُونَ تِمُواْتِ، طَنْ وَتَ بَيَهُودِيَ مَيْبِے؞ بَابَنْسَ كُوَ بَهٜىٰلٜىٰنٜىٰ نٜىٰ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai kuma Bulus ya zo Darba da Listira. Akwai wani almajiri a Listira, mai suna Timoti, ɗan wata Bayahudiya mai bi, ubansa kuwa Bahelene ne.