Acts 16:14 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ɗaya daga cikin waɗanda suka saurare mu mace ce mai suna Lidiya, mai sayar da yadunan jan garura masu tsada daga birnin Tiyatira, mai yi wa Allah sujada. Ubangiji ya buɗe zuciyarta har ta karɓi saƙon Bulus.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
أَݣَويْ وَتَ مَثٜىٰ مَيْ سُونَ لِدِيَ، مَيْ بَوْتَرْ اللَّهْ ، تَنَ سَوْرَرُوانْمُ؞ عِتَ یَرْ غَرِنْ تَيَتِرَ ثٜىٰ، تَنَ سَيَرْ دَ يَدُنَنْ جَرْ غَرُورَا مَاسُ ڟَادَ؞ عُبَنْغِجِ يَبُوطٜىٰ ذُوثِيَارْتَ، حَرْ تَسَا حَنْكَلِ تَسَوْرَرِ أَبِنْدَ بُلُسْ يَڢَطَا؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ɗaya daga cikin masu sauraronmu wata mace ce, mai suna Lidiya, mai sayar da jar hajja, mutuniyar Tayatira, mai ibada ce kuma. Ubangiji ya buɗe zuciyarta, har ta mai da hankali ga abin da Bulus ya faɗa.