Acts 16:18 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ta yi ta faɗin haka har kwanaki masu yawa. A ƙarshe Bulus ya damu ƙwarai sai ya juya ya ce wa aljanin, “A cikin sunan Yesu Kiristi na umarce ka, ka rabu da ita!” Nan take aljanin ya rabu da ita.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
تَايِ تَيِنْ حَكَ ݣُونَكِے دَيَوَ؞ سَيْ بُلُسْ يَٻَاتَ رَيْ سُواْسَيْ، يَجُويَ يَثٜىٰ وَ أَلْجَنِنْ «نَعُمَرْثٜىٰكَ ثِكِنْ سُونَنْ عِيسَىٰ أَلْمَسِيحُ ، كَرَبُ دَ عِتَ؞» نَنْ تَكٜىٰ كُوَ يَرَبُ دَ عِتَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Haka ta dinga yi kwana da kwanaki, har Bulus ya ji haushi ƙwarai, ya juya ya ce wa aljanin, “Na umarce ka da sunan Yesu Almasihu, ka rabu da ita.” Nan take kuwa ya rabu da ita.