Acts 18:27 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’ad da Afollos ya so ya tafi Akayya, sai ’yan’uwa suka ƙarfafa shi suka kuma rubuta wa almajiran da suke can da su marabce shi. Da isowarsa, ya zama da taimako ƙwarai ga waɗanda ta wurin alheri suka gaskata.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دَ أَڢُواْلُّواسْ يَسُواْ يَڧٜىٰتَرٜىٰ ذُوَا ڧَسَرْ عَكَيَ، مَاسُبِے سُكَ تَيْمَكٜىٰشِ؞ سُكَ رُبُوتَ وَمَاسُبِے نَ عَكَيَ وَسِيڧَ دُواْمِنْ سُكَرْٻٜىٰشِ حَنُّ بِيُ بِيُ؞ دَ يَكَيْ ثَنْ كُوَ يَذَمَ دَ تَيْمَكُواْ سُواْسَيْ غَ وَطَنْدَ سُكَ بَادَ غَسْكِيَ تَوُرِنْ أَلْحٜىٰرِنْ اللَّهْ ،
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Da ya so hayewa zuwa ƙasar Akaya, 'yan'uwa suka taimake shi, suka rubuta wa masu bi wasiƙa su karɓe shi hannu biyu biyu. Da kuwa ya isa, ya yi matuƙar taimako ga waɗanda suka ba da gaskiya ta wurin alherin Ubangiji,