Acts 19:13 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Waɗansu Yahudawa masu yawo gari-gari suna fitar da mugayen ruhohi suka yi ƙoƙari su yi amfani da sunan Ubangiji Yesu a kan waɗanda suke da aljanu. Suna cewa, “A cikin sunan Yesu wanda Bulus yake wa’azi, na umarce ku, ku fito.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ وَطَنْسُ يَهُودَاوَا مَاسُ يَٰوُاْ غَرِ غَرِ سُنَ ڢِتَرْدَ مُوغَيٜىٰنْ رُوحُواْحِ سُكَيِ ڧُواْڧَرِ سُيِ أَمْڢَانِ دَ سُونَنْ عُبَنْ‌غِجِ عِيسَىٰ عَكَنْ مَاسُ مُوغَيٜىٰنْ رُوحُواْحِ؞ سُنَ ثٜىٰوَ «نَا عُمَرْثٜىٰكُ دَ سُونَنْ عِيسَىٰ نَّنْ دَ بُلُسْ يَكٜىٰ وَعَظِنْسَ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai waɗansu Yahudawa masu yawo gari gari, matsubbata, suka yi ƙoƙarin kama sunan Ubangiji Yesu ga masu baƙaƙen aljannu, suna cewa, “Mun umarce ku da sunan Yesun nan da Bulus yake wa'azi.”

Recommended Reading