Acts 19:21 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Bayan dukan wannan ya faru, sai Bulus ya yanke shawara ya ratsa Makidoniya da Akayya in za shi Urushalima. Ya kuma ce, “Bayan na tafi can, dole in ziyarci Roma ita ma.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
بَايَنْ وَطَنَّنْ أَبُبُوَ، بُلُسْ يَشِرْيَ أَ رَنْسَ ثٜىٰوَ عِدَنْ يَا ظَظْذَاغَ ڧَسَرْ مَكِدُواْنِيَ دَ تَ عَكَيَ، ذَيْجٜىٰ عُرُوشَلِيمَ؞ يَكُمَثٜىٰ «بَايَنْدَ نَتَڢِے ثَنْ كُوَ دُواْلٜىٰنٜىٰ إِنْجٜىٰ إِنْ غَا بِرْنِنْ رُواْمَ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Bayan waɗannan al'amura Bulus ya ƙudura a ransa, cewa in ya zazzaga ƙasar Makidoniya da ta Akaya, za shi Urushalima, ya kuma ce, “Bayan na je can, lalle ne kuma in je in ga birnin Roma.”