Acts 21:11 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Da ya zo wurinmu, sai ya ɗauki ɗamarar Bulus, ya ɗaura hannuwansa da ƙafafunsa da ita sa’an nan ya ce, “Ruhu Mai Tsarki ya ce, ‘Haka Yahudawan Urushalima za su daure mai wannan ɗamara su kuma ba da shi ga Al’ummai.’ ”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دَ أَغَبُسْ يَذُواْ وُرِنْمُ، سَيْ يَطَوْكِ طَمَرَ تَ بُلُسْ؞ سَيْ شِ أَغَبُسْ يَطَوْرٜىٰ حَنُّوَنْسَ دَ ڧَڢَاڢُنْسَ يَثٜىٰ «غَا أَبِنْدَ رُوحُ مَيْ ڟَرْكِے يَثٜىٰ، ‹حَكَ يَهُودَاوَنْ عُرُوشَلِيمَ ذَاسُ طَوْرٜىٰ مَيْ طَمَرَرْ نَنْ، سُكُمَ بَادَشِ غَ وَطَنْدَ بَا يَهُودَاوَا بَ؞› »
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Da ya zo gare mu, ya ɗauki ɗamarar Bulus ya ɗaure kansa sawu da hannu, ya ce, “Ga abin da Ruhu Mai Tsarki ya ce, ‘Haka Yahudawan Urushalima za su ɗaure mai wannan ɗamara, su kuma bashe shi ga al'ummai.’ ”